Osun ta yi asarar biliyoyin Naira ta hanyar hako ma’adinai ba bisa ka’ida ba – Adeleke


Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke ya bayyana cewa jihar ta yi asarar biliyoyin Naira da ya kamata a ce ta samu a matsayin kudin shiga ga masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba.

Ya yi zargin cewa gwamnatin da ta gabata ta Adegboyega Oyetola ta barnatar da albarkatun kasa a yadda aka gudanar da aikin samar da ruwan sha na Ilesa.

Gwamna Adeleke ya bayyana haka ne yayin da yake jawabi ga ma’aikatan ilimi da wadanda ba na ilimi ba a yayin wata ziyarar bazata da ya kai a Kwalejin Ilimi ta Jihar Osun da ke Ilesa a ranar Juma’a.

A jawabinsa yayin ziyarar, gwamnan ya yi amfani da damar wajen sanar da al’ummar Ijesha aikin samar da ruwan sha na Ilesa da kuma illolin da ayyukan hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a yankin a karkashin gwamnatin da ta gabata dangane da gurbatar ruwa, gurbacewar muhalli da kuma matsalar rashin samun kudin shiga.

Batun hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba da kuma inganta kwalejin ilimi ta Ilesa, ya kasance abin cece-kuce tsakanin gwamnatin Adeleke da gwamnatin Adegboyega Oyetola mai barin gado.

A cikin kalamansa, “Gwamnatin APC da ta shude ta gudanar da aikin samar da ruwan sha a garin Ilesa da yadda aka kashe sama da naira biliyan 12 ba tare da wani sakamako ba.

“Na gana da Ministan Albarkatun Ruwa wanda ya tabbatar mani da cewa aikin ya faskara saboda ayyukan damfarar dan kwangilar. Sanin al’umma ne kuma mai ba da shawara kan aikin ruwa ya yi zargin neman dala miliyan biyar daga kwamitin majalisar jiha kan albarkatun ruwa.”

“Tun daga lokacin ne muka kafa kwamitin hadin gwiwa da ma’aikatar albarkatun ruwa. Za a sake tallata kwangilar bayan an sasanta ba tare da kotu ba tare da duk masu ruwa da tsaki a aikin,” in ji Gwamnan.

Gwamnan wanda ya dage cewa gwamnatin APC da ta shude ta karfafa ayyukan hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a Ijesha da kewaye, ya kara da cewa lamarin ya janyo mummunar gurbacewar muhalli da gurbatar ruwa a jihar tare da hana jihar samun kudaden shigar da ake bukata daga ayyukan hakar ma’adinai.

“Gwamnatin APC ta karfafa ma’adanai ba bisa ka’ida ba a jihar. Hakan ya jawo gurbacewar ruwan mu sosai. Ministan Ruwa ya tabbatar min da cewa majiyar ruwan dake Ilesa ta gurbace.

“Jihar ta kuma yi asarar biliyoyin Naira da ya kamata a samu a matsayin IGR idan har an yi aikin hakar ma’adanai yadda ya kamata.

“Kwamitin da na kafa domin duba ayyukan masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba sun mika rahotonsu a jiya. Zan bi ta kuma nan ba da jimawa ba zan fitar da dabarun da gwamnatina za ta yi amfani da su wajen magance gurbatar ruwa da muhalli da ayyukan hakar ma’adinai ke haifarwa.

“Ina da yakinin cewa hakan zai kawar da kura-kurai da gwamnatin APC ta haddasa a yankin Ijesha,” in ji gwamnan.

Adeleke da ya hau kujerar gwamna a watan Nuwamba, 2022 ya kwace lasisin hakar gwal da aka baiwa kamfanonin hakar ma’adinai a jihar.

Har ila yau, an dakatar da mashawarcin da ke kula da aikin samar da ruwa na Ilesa.

A cikin makon nan ne dai jam’iyyar APC ta Osun ta yi zargin cewa Adeleke ya dakatar da aikin samar da ruwan sha na Ilesa ba bisa ka’ida ba wanda ya kai dala miliyan 106.





Source link

Leave a Comment