Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo ya lashe zaben kujerar tsohon gwamnan jihar Sanata Rasidi Adewolu Ladoja.
Makinde wanda ke neman wa’adi na biyu a jam’iyyar PDP ya samu kuri’u 98 inda ya doke sauran ‘yan takarar.
Dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Teslim Folarin, ya samu kuri’u 35.
A ranar Asabar ne dai aka gudanar da zabukan gwamnoni da na ‘yan majalisar jiha a dukkanin kananan hukumomin jihar 33.